News
Kotu ta yankewa Zakara hukuncin kisa a KANO
Wata kotun Majasteri da ke da zama a gidan Murtala a birnin Kano, ta umarci wani mutum mai suna Isyaku Shu’aibu, mazaunin unguwar Ja’en da ya yanka Zakaransa.
Tun farko dai wani maƙwafcinsa ne mai suna Malam Yusuf Muhammad Ja’en, ya shigar da ƙara gaban Kotun, yana mai cewa, Zakaran yana shiga haƙƙinsa ta hanyar hana shi barci da yawan Cara.
Amma koda aka karantowa wanda ake ƙara, sai ya ce, gaskiya ne Zakaran nasa na yawan yin Cara, kuma zai yanka shi ne a bikin “Good Friday” don haka ya roƙi Kotun da ta sahale masa zuwa ranar.
Mai shari’a Halima Wali ta amince inda ta umarci mutumin da ya killace Zakaran kuma ya yanka shi a ranar Juma’a mai zuwa wato ranar “Good Friday” ɗin.
-
News4 days agoShekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano
-
News6 days agoKamfanonin Bada Bashi Ne Suka Cire N1.5bn Daga Albashin Ma’aikatan Kano — SSG
-
News5 days agoDr. Muhammed Musa Zango Ya Kaddamar Da Neman Takarar Sanatan Kano Ta Tsakiya A Jam’iyyar APC
