News
Majalisa: Kudirin haramtawa likitocin Najeriya aiki a waje
Wani kudirin doka da zai hana likitocin Najeriya ficewa daga kasar har sai sun yi aikin tsawon shekaru 5 a cikin gida, ya tsallake karatu na biyu a majalisar wakilai.
Manufar dokar itace dakile karuwar adadin likitocin dake ficewa aiki waje, bisa kwadaituwa da kyakkyawan yanayi.
Mamba a majalisar, Ganiyu Abiodun Johnson ne ya dauki nauyin kudirin, wanda aka yi wa take da ‘kudirin yiwa dokar likitoci ta 2004 kwaskwarima’.
NAHCO ta fitar da kudin aikin Hajjin bana ga jahohin yankin Arewa.
Johnson yace zai fi kyautuwa likitocin su fara amfanar da cikin gida da kwarewar da suka samu karkashin kulawar kasa, akalla da shekaru 5 kafin su fice.
Zaman majalisar na ranar Alhamis, 6 ga watan Aprilu, karkashin jagorancin Femi Gbajabiamila ya amince da wannan kudiri a karatu na biyu.
-
News4 days agoShekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano
-
News6 days agoKamfanonin Bada Bashi Ne Suka Cire N1.5bn Daga Albashin Ma’aikatan Kano — SSG
-
News5 days agoDr. Muhammed Musa Zango Ya Kaddamar Da Neman Takarar Sanatan Kano Ta Tsakiya A Jam’iyyar APC
