News
Gwamnati Za Ta Binne Gawarwaki 49 A Rami Guda A Kaduna
Gwamnatin Jihar Kaduna ta ce za ta binne wasu gawarwaki 49 a rami daya idan ’yan uwan masu su ba su zo sun tafi da su ba.
Gwamnatin ta ce za ta yi hakan ne bayan wa’adin kwana biyar da ta ba wa dangin mamatan su dauke su daga mutuwarin Babban Asibitin Sabon Tasha da ke Karamar Hukumar Chikun ta jihar.
Shugaban Karamar Hukumar Chikun, Salasi Nuhu Musa, ya ce an kai gawarwakin asibitin ne a lokuta daban-daban daga ofishin ’yan sanda na Kasuwar Magani da kuma na Toll Gate.
A cewarsa, “An iya gane 25 daga cikin gawarwakin 49, ragowar 24 kuma ba a gane su ba saboda ba sa dauke da wata alamar shaida a lokacin da aka kawo su mutuwarin.
Ya kara da cewa tuni karamar hukumar ta samu amincewar gwamnatin jihar domin binne gawarwakin, wanda zai gudana a mako mai zuwa.
-
News5 days ago
ICPC Ta Yi Barazanar Daurin Shekaru 7 Ga Masu Yiwa Baki Rajistar NIN A Matsayin Yan Najeriya
-
News1 day ago
Jam’iyyar ADC Ta Yi Watsi Da Cire Ta Daga Rijista, Ta Sha Alwashin Kalubalantar Hukuncin Kotu
-
News6 days ago
Hayar Jirage Hadi Sirika Ya Dakko Daga Habasha Don Damfarar Yan Najeriya Da Sunan “Nigeria Air” — Shaida
