Connect with us

News

Sojoji Sun Harbe Barawon Akwatin Zabe A Kebbi

Published

on

 

Sojojin da ke sintirin jiran ko ta kwana sun harbe wani mutum yana kokarin kwace akwatin zabe a hannun jami’an Hukumar Zabe ta Kasa INEC a Jihar Kebbi.

Advertisement

 

Lamarin na wannan Asabar din da ake karasa Zaben 2023 a wasu sassan jihar ya faru ne a rumfar zabe mai lamba 001 a mazabar Bajida da ke Kudancin Jihar Kebbi.

Advertisement

 

 

Advertisement

Bayanai da ke fitowa daga mazauna yankin na cewa marigayin guda ne daga cikin haramtacciyar kungiyar ‘yan sa kai da ke yankin Zuru a jihar.

Sojojin Sudan na fafatawa da dakarun RSF

Wakilinmu ya ruwaito cewa, karar kwana ta cimma mutumin ne wanda ya kutsa cikin rumfar zaben yana mai ikirarin cewa shi jami’in tsaro ne, inda ake zargin har ya yi yunkurin karbar bindigar wani soja a rumfar zaben.

Advertisement

 

 

Advertisement

Sai dai wasu mutanen yankin sun yi zargin cewa wakilin jam’iyyar PDP ne.

 

Advertisement

Wasu kuma dai sun bayyana cewa mutumin tare da wasu masu neman tayar da zaune tsaye sun kutsa rumfar zaben ne suna kokarin kwace akwatunan zabe daga hannun jamian INEC da ke shirin tafiya cibiyar tattara sakamako.

 

Advertisement

Sai dai kokarin da mutanen wurin suka yi na dakatar da shi ya ci tura, inda ya yi yunkurin karbar bindigar wani soja wanda babu wata-wata wani sojan ya gaggauta diga masa harsashi farat daya.

 

Advertisement

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending