Connect with us

News

Wani Matashi Ya Gudu Da Budurwar Mahaifinsa Mako Uku Kafin Daura Musu Aure

Published

on

 

 

Advertisement

Wani matashi mai suna Ahmed Golo mai shekara 24 ya gudu da wata budurwa mai suna Sa’ada Mohammed mai shekara 18 a duniya da mahaifinsa Ishmael Golo mai shekara 71 yake shirin ya aura bayan Sallah da mako daya, inda ya ce budurwar ta yi wa mahaifinsa nasa yarinta.

 

Advertisement

Lamarin ya auku ne a kauyen Magarjali da ke Gundumar Tana Riber a kasar Kenya kamar yadda jaridar The Nation ta Kenya ta ruwaito a ranar Alhamis din makon jiya.

. Yan sanda sun kama fasto kan yi wa mabiyansa fatawar yin azumin ganin Yesu

 

Advertisement

Wani daga cikin ’yan uwan Mista Golo mai suna Hassan Wario ya ce, dattijon ya riga ya shirya da budurwar har ya biya sadakinta, inda aka yanke shawarar daura musu aure a bayan azumi.

 

Advertisement

Ya amince shi da iyayen budurwar cewa a bar bikin aurensu sai bayan Karamar Sallah da mako daya, amma sai ’ya’yansa suka turje suka ce matar da zai aura ba ta kai autarsa a shekaru ba, don haka suka nemi ya sake shawara.

 

Advertisement

 

Mista Wario ya ce duk kokarin da aka yi don shawo kan ’ya’yan Mista Golo su amince da zabin mahaifinsu ba a cim ma nasara ba, wanda hakan ya jawo takaddama a cikin iyalan.

Advertisement

 

Ya ce, “Mun yi kokarin jawo hankalinsu amma suka ki. Hatta mahaifiyarsu ta yi kokarin kwantar musu da hankali amma suka yi kunnen kashi, musamman ’ya’yansa mata.”

Advertisement

 

Bayan kasa shawo kan ’ya’yan ne sai babban dan matarsa ta biyu ya yanke shawarar gano inda amarya mai jiran ranar take, inda ya gudu da ita.

Advertisement

 

 

Advertisement

A ranar Talatar makon jiya da mutane suke kokarin zuwa masallaci ne Ahmed da Sa’ada suka gudu inda suka bar rubutaccen sako ga mahaifinsa suna ba shi shawarar ya nemi mace daidai da shi ya bar kananan ’yan mata ga ’ya’yansa maza.

 

Advertisement

 

“Da misalin karfe 10 na safe ne muka fahimci ba ta nan, saboda ba mu gan ta ba, sai muka gano wani rubutu da harshenmu amma ba rubutunta ba ne,” in ji ’yar uwar Sa’ada mai suna Asha Fadhe.

Advertisement

 

Washegari Laraba, Ahmed ya kira gida ya yi magana da mahaifiyarsa ya shaida mata cewa ba zai bari mahaifinsu ya zubar da mutuncin gidansu ba.

Advertisement

 

Mahaifiyar ta ce Ahmed ya ce lokacin da tsofaffi za su rika auren jikokinsu ya wuce, inda ya bukaci mahaifinsa ya nemi wata madaidaiciya ya aura.

Advertisement

 

“Ya ce, zai auri yarinyar su hayayyafa kafin ya dawo gida. Na yi kokarin shaida masa hakan bai dace ba, amma ya ce budurwar ta yarda kuma yana farin ciki ya kubutar da ita,” in ji ta.

Advertisement

 

 

Advertisement

Iyalan gidan su Sa’ada sun ce ta sanar da su cewa tana nan lafiya. Sun ce ta shaida musu cewa, ba ta son auren Mista Golo inda ta ce ya yi mata tsufa kuma zai fi kyau ta auri matashi.

 

Advertisement

Sai dai Mista Golo ya zargi uwargidansa da matarsa ta uku da tunzura ’ya’yansa su ki amincewa da auren nasa, inda ya ce su ne suka kisa wannan badakala.

 

Advertisement

Tuni ya bukaci iyayen budurwar su dawo masa da sadakinsa, inda ya ce sai su je su nemi sabon sadaki a wajen dansa.

 

Advertisement

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending