News
Ina Mamakin Yafewa Buhari da Ganduje – Mu’azu Magaji
Tsohon Kwamishinan ayyuka na jihar Kano karkashin Gwamnatin Dr. Abdullahi Umar Ganduje, Engr. Mu’azu Magaji Dan Sarauniya ya bayyana mamakin sa kan kalaman da manyan shugabanni ke yi na neman yafiyar al’umma a baya-bayan nan.
Kalaman shugaba Buhari na zuwa ne bayan Gwamna Ganduje ya nemi makamancin hakan cikin makon da ya gabata.
Hakan na kunshe ne ta cikin wani sako da Dan sarauniyar ya wallafa shafin,sa na sadarwar Facebook.
Dan sarauniyar ya wallafa rubutan a shafansa kamar haka’Wato Ina jinjina yafewa Ganduje da Buhari a lokaci guda.
Ni dai na barwa Allah ya duba lamarin…in sun cancanci Yafiya a binda suka aikata.’
Nan ba da dadewa bane za’a sami sauyin Gwamnatoci cikin wata mai kamawa na Mayu.
-
News1 day ago
Ba Za Mu Yi Wa Kowa Rangwame Ba A Wajan Yaƙi Da Sha Da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi Ba — Muhyi Magaji
-
News2 days ago
Ana Zargin Matar Aure Da Shaƙe ’Yar Kishiyarta Mai Shekara 3 Har Lahira
-
News6 days ago
KANO: Yara 24 Da Ake Tuhuma Da Laifi Sun Amfana Da Shirin Gyaran Tarbiya Maimakon Hukuncin Kotu A Watan Yuli
