Connect with us

News

An kashe mutane fiye da 500 a Kudancin Kaduna cikin shekara 6

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

Advertisement

 

Shugaban Ƙungiyar ci gaban al’ummar Atyap a jihar Kaduna, Mista Samuel Achi ya bayyana cewa daga shekarar 2017 zuwa yanzu, an kashe mutum 518 sannan dubbai sun tsere, an kuma ɗaiɗaita ƙauyuka 20 yayin da aka ƙone wasu ƙauyukan 18 a Kudancin Kaduna.

Advertisement

 

Shugaban ya bayyana haka ne a wani taron manema labarai da aka gudanar a yau a Samaru Kataf. Ya ce hare-haren da ake ci gaba da kai wa sun yi kamanceceniya da waɗanda aka kai a 2019 kuma wasu ɓatagari ne suke kai wa waɗanda kuma ya kamata a ce hukumomin tsaro sun hukunta su.

Advertisement

JAMB Ta Sanya Ranar Fitar da Sakamakon Jarabawar UTME 2023

Jaridar Punch ta rawaito Mista Achi na “kira ga al’ummarmu da su kare kansu daga duk wasu hare-hare,” in ji shi inda ya ce an kai maƙura.

 

Advertisement

Da yake kokawa kan zargin da ake cewa sojoji na da hannu, Mista Achi ya ce sojojin da aka tanada domin tabbatar da tsaro a yankin, ba sa yin wani abu na kawo sauƙi.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending