Connect with us

Uncategorized

Sudan: An kashe fiye da mutum 100 a yankin Darfur

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN

 

Mummunan faɗa ya ɓarke a yankin Darfur na ƙasar Sudan, yayin da rahotonni ke cewa fiye da mutum 100 aka kashe a birnin El Geneina.

Advertisement

Wannan na zuwa ne kwanaki bayan wakilan ɓangarorin da ke yaki da juna a ƙasar sun amince da kare fararen hula tare da barin kayan agaji kaiwa zuwa gare su.

Mutum biyu sun yi ba-hayar ƙulli 193 na hodar ibilis a hannun NDLEA

Kungiyar kare haƙƙin bil-dama a yankin na Darfur ta ce babban limamin birnin El Geneina na daga cikin gwamman mutanen da suka mutu a rikicin da ya ɓarke a birnin.

Advertisement

Hotuna sun nuna yadda gine-gine suka lalace bayan da aka yi musu ruwan hare-hare da ta sama.

Ana zargin wata ƙungiyar Larabawa mai alaƙa da dakarun RSF da ƙaddamar da hare-hare kan gidaje a birnin.

Advertisement

Kusan shekara 20 bayan kisan kiyashin da aka tafka a yankin, har yanzu Darfur na ci gaba da fuskantar rikice-rikice.

Kungiyoyin bayar da agaji na ci gaba da janyewa yayin da cibiyoyin lafiya suka kasance a rufe, sakamakon faɗan da ya ɓarke a tsakanin sojojin ƙasar da dakarun RSF.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending