Connect with us

News

Jami’in hukumar EFCC Ya Mutu A Wurin Fada Da Abokan Aikinsa

Published

on

Wani jami’in Hukumar Yaki da Masu Karya Tattalin Arziki (EFCC) ya rasa ransa a wani fada da ya barke tsakaninsa a abokan aikinsa a Jihar Sakkwato.

Kakakin hukumar EFCC, Wilson Uwujaren, ya bayyana cewa wasu jami’an hukumar gudu uku sun kaure da fada ne bayan takkada ta ta barke tsakaninsu a kan ajiyar wasu kaya.

Advertisement

Kotu ta yankewa mutum uku hukuncin kisa kan satar waya da kamfuta

Ya ce likitoci a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Usmanu Danfodio da ke Sakkwato ne suka tabbatar da rasuwar jami’in mai suna Sufeto Abel Isah Dickson a ranar 7 ga watan Mayu da muke ciki.

Da yake sanar da hakan a safiyar Talata, Uwujaren ya ce sauran mutum biyun na tsare a hannun ‘an sanda, bayan aukuwar lamarin a ranar 5 ga watan Mayun da muke ciki.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending