News
Gambari Ya Mika Wa Gbajabiamila A Matsayin Shugaban Ma’aikata
DAGA KAIRU BASIRU FULTAN
Shugaban ma’aikatan tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari, Ibrahim Gambari, ya mikawa kakakin majalisar wakilai mai barin gado, Femi Gbajabiamila, ragamar mulki
Gambari ya rike mukamin daga 2020 zuwa 2023 bayan rasuwar magabacin sa Abba Kyari a watan Afrilun 2020.
Zaman wanda ya baje kolin takardar mika mulki ya gudana ne a ranar Litinin a fadar shugaban kasa da ke Abuja kuma shugaban kasa Bola Tinubu ya halarta.
Majalisar Dattawa ta amince da bukatar Tinubu ta nada mashawarta na musamman guda 20
A makon da ya gabata ne Tinubu ya bayyana nadin Gbajabiamila a matsayin shugaban ma’aikatan fadarsa, yayin da Sanata Ibrahim Hassan Hadejia, wanda tsohon mataimakin gwamnan jihar Jigawa ne aka nada a matsayin mataimakin shugaban ma’aikata.
Jim kadan bayan shugaban kasar ya nada Gbajabiamila a hukumance, dan shekaru 60 da haihuwa ya bayyana jin dadinsa a wata sanarwa da ya kawo karshen cece-kuce na makonni.
“Bayan shafe shekaru 20 da suka gabata a majalisar dokokin Najeriya, kuma bayan na lashe zabe karo na 6 a majalisar dokokin kasar, zan yi aiki tare da shugaban kasa wajen sauke babban aikin da ke gabansa domin zaman lafiya da ci gaban tarayyar Najeriya.
“Zan ba da mafi kyawuna lokacin da na hau ofis a ranar 14 ga Yuni 2023 kamar yadda aka nuna a cikin wasikar shugaban kasa,” in ji shi.
A matsayinsa na shugaban ma’aikata, Gbajabiamila ya fi mayar da hankali ne kan tafiyar da harkokin yada labarai da jama’a, yayin da yake ba shugaban kasa shawara kan batutuwa daban-daban.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
