News
Gwamnati Ta Ayyana Litinin A Matsayin Ranar Hutu
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADIN
Gwamnatin Tarayya ta ayyana Litinin, 12 ga watan Yuni, a matsayin ranar hutu albarkacin Ranar Dimokuradiyya ta bana.
Babban Sakataren Ma’aikatar Al’amuran Cikin Gida, Dokta Oluwatoyin Akinlade, ne ya tabbatar da hakan a cikin wata sanarwa ranar Alhamis.
Baya ga taya ’yan Najeriya murna, sanarwar ta ce kamar sauran kasashe, Dimokuradiyyar Najeriya ta yi fama da nasarori da kuma tarin kalubale.
Ta kuma ce, “Amma babban abin birgewar shi ne Najeriya, a matsayinta na kasa da kuma mutanenta sun tsaya tsayin daka wajen ganin ginshikan Dimokuradiyya sun tabbata.
“A wannan rana mai cike da tarihi, muna gayyatar ’yan Najeriya da kawayen kasar su zo su taya mu murnar ci gaban da muka samu sannan a duba hanyoyin da za abi wajen ciyar da Dimokuradiyyar gaba,” in ji sanarwar.
Tsohon Shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari ne dai ya sauya ranar Dimokuradiyyar zuwa ranar ta 12 ga watan Yuni.
A baya dai, ana bikin ne a ranar 29 ga watan Mayu.
-
News2 days ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News2 days ago
Zaben 2027: INEC Ta Amince Da Atiku Abubakar, ‘Yan Takarar ADC 470
