Connect with us

News

Gwamnati Ta Ayyana Litinin A Matsayin Ranar Hutu

Published

on

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADIN

 

Advertisement

Gwamnatin Tarayya ta ayyana Litinin, 12 ga watan Yuni, a matsayin ranar hutu albarkacin Ranar Dimokuradiyya ta bana.

Babban Sakataren Ma’aikatar Al’amuran Cikin Gida, Dokta Oluwatoyin Akinlade, ne ya tabbatar da hakan a cikin wata sanarwa ranar Alhamis.

Advertisement

 

KANO:An Gurfanar Da Wani Matashi a Gaban Kotun Shari’ar Musulunci Bisa Zargin Sace Lasifikar Masallaci

Baya ga taya ’yan Najeriya murna, sanarwar ta ce kamar sauran kasashe, Dimokuradiyyar Najeriya ta yi fama da nasarori da kuma tarin kalubale.

Advertisement

Ta kuma ce, “Amma babban abin birgewar shi ne Najeriya, a matsayinta na kasa da kuma mutanenta sun tsaya tsayin daka wajen ganin ginshikan Dimokuradiyya sun tabbata.

“A wannan rana mai cike da tarihi, muna gayyatar ’yan Najeriya da kawayen kasar su zo su taya mu murnar ci gaban da muka samu sannan a duba hanyoyin da za abi wajen ciyar da Dimokuradiyyar gaba,” in ji sanarwar.

Advertisement

Tsohon Shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari ne dai ya sauya ranar Dimokuradiyyar zuwa ranar ta 12 ga watan Yuni.

A baya dai, ana bikin ne a ranar 29 ga watan Mayu.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending