Connect with us

Politics

Gwamnan Kano Ya Nada ‘Dansa’ Shugabancin Wata Hukumar Gwamnati

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN

 

Advertisement

 

Gwamnan  Kano, Abba Kabir Yusuf ya naɗa ɗansa na riƙo, Ahmad A. Yusuf a matsayin Sakataren Gudanarwa na Hukumar Tarihi da Al’adu ta jihar.

Advertisement

Ahmad A. Yusuf ɗa ne ga shaƙiƙin gwamnan, amma  a hannunsa ya taso har ma ake masa kallon ɗansa na fari.

Idan za a iya tunawa dai, lokacin da gwamnan ke karɓar satifiket na nasarar zaɓensa daga hukumar zaɓe, INEC ranar 29 ga Maris, 2023, gwamnan ya bada tabbacin cewa ba zai sa iyalinsa cikin harkokin mulki ba.

Advertisement

Na samu goran gayyata na musamnan daga Majalisar dinkin duniya – Malam Shekarau.

“Babu yadda za a yi in bar iyalina su tsoma baki a harkokin gwamnati ba, saboda ni kaɗai na rantse ba tare da su ba, wato dai su babu su a gwamnati,’” in ji Gwamnan.

Sai dai, a wata sanarwa da Kakakin Gwamna, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar ranar Lahadi, Gwamnan ya sanar da naɗa ɗan na sa a muƙamin gwamnati.

Advertisement

Sanarwar ta ce ” Gwamnan jihar Kano Mai girma Alhaji Abba Kabir Yusuf ya amince da naɗin waɗanann: Arc. Ahmad A. Yusuf, Sakataren Gudanarwa, Hukumar Tarihi da Al’adu ta jihar Kano; Engr. Ado Jibrin Kankarofi, Mataimakin Manajan Darakta, Hukumar Kula da Hanyoyi ta jihar Kano (KARMA), Hauwa Muhammad, Mataimakiya ta Musamman, Harkokin Mata.

“Duk waɗannan naɗe-naɗe sun fara aiki nan take, ” kamar yadda sanarwar ta ƙunsa.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending