Connect with us

News

Wata Kungiya Na Zargin Gwamnatin Kano Da Yunkurin Bata Alakar Ganduje Da Sgugaban Kasa Tinubu

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU  FULATAN

 

Advertisement

Gamayyar kungiyoyin farar hula na Arewa sunyi gargadi kan yunkurin da gwamnatin jihar Kano ke  shiryawa na yiwa tsohon gwamna Abdullahi Umar Ganduje ‘keta.

Kungiyar ta ce akwai wata makarkashiya  da gwamnatin jihar ta shirya na bata sunan Ganduje ta hanyarsiyasa da hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta jihar Kano.

Advertisement

Ba ka isa ka karɓe mana gurbin muƙamin minista ba, APC ta faɗawa Wike

A cikin wata sanarwa da sakataren kungiyar Muhammed Lawan Shuaibu ya fitar, kungiyar ta nunar da cewa ana  yunkurin ne domin bata sunan tsohon gwamnan da ke da kyakkyawar alaka da shugaban kasa  Bola Ahamed Tinubu.

Kungiyar da ke karkashin kungiyar kungiyar rajin tabbatar da shugabanci Nagari ta kuma yi ikirarin cewa gwamnatin Kano ta dauki matakin ne domin hana Ganduje samun mukaman siyasa a matakin tarayya.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending