News
An Kori Manyan Ƴansanda 3 Da Rage Matsayin Guda 9 Bisa Laifin Rashin Ɗa’a
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Hukumar kula da Ayyukan Ƴansanda, PSC, ta amince da korar wasu manyan jami’an ƴansanda uku bisa laifukan rashin da’a da kuma zubar da kimar aikin.
Kakakin hukumar Ikechukwu Ani ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar a jiya Lahadi a Abuja.
Umarnin Da Kotu Ta Bayar Akan Hana Kama Ganduje, Na Wucin Gadi Ne – Lauya
Ya ce hukumar ta kuma amince da rage matsayin wasu jami’ai su tara da suka hada da kwamishinan ƴansanda.
A cewarsa, hukumar ta dauki wannan matakin ne a yayin taronta na 21, karkashin jagorancin mai shari’a Clara Ogunbiyi, kwamishiniyar shari’a a hukumar.
Mista Ani ya ce Ms Ogunbiyi ce ta jagoranci taron a madadin shugaban PSC, Solomon Arase, wanda daga baya ya shigo taron, wanda aka gudanar ta manhajar Zoom.
Kakakin na PSC ya ce hukumar ta kuma amince da ritayar dole ta wani mataimakin kwamishinan ƴansanda, tare da bayar da umarnin a mayar da duk hakkokin sa da aka biya shi bisa kuskure.
Ya kara da cewa hukumar ta amince da karin girma ga marigayi Insp. Ifeanyi Oroke, zuwa matsayi na gaba na Mataimakin Sufurtandan ƴansanda 2..
Sai dai kuma Mista Ani ya ce hukumar ta kuma maido da wani jami’in da aka kora bisa kuskure, Insp. Augustina Oko, inda ya kara da cewa dawiwar ta ta aiki ta fara tun daga ranar da aka kore ta.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
