News
Kotu ta umurci hukumar DSS da ta gurfanar da Emefiele ko kuma ta saki shi cikin kwanaki bakwai
Advertisements

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Kotu ta umurci hukumar DSS da ta gurfanar da Emefiele ko kuma ta saki shi cikin kwanaki bakwai.
Mai shari’a Hamza Muazu na babbar kotun birnin tarayya Abuja ya umurci hukumar tsaro ta farin kaya ta (DSS) da ta gurfanar da tsohon gwamnan babban bankin Najeriya CBN Godwin Emefiele a kotu cikin mako guda ko kuma a sake shi.
Kotu ta umurci hukumar DSS da ta gurfanar da Emefiele ko kuma ta saki shi cikin kwanaki bakwai
Lauyan Emefiele, Joseph Dawodu, Babban Lauyan Najeriya (SAN) ya ce za a aiwatar da bukatar neman belin tare da fatan za a ba da shi.
Advertisements
