News
An sace Sakataren Jam’iyyar APC a Jahr Kaduna
DAGA MIUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
An sace Sakataren Jam’iyyar APC, Hon. Kawu Ibrahim Yakasai a jihar Kaduna.
An sace Yakasai wanda tsohon Shugaban karamar hukumar Soba ne a gidansa da ke kauyen Yakasai da misalin karfe 10:00 na daren ranar Juma’a.
Rahotanni na nuni da cewa ‘yan bindigan sun kai hari ne musamman a gidansa inda suka dauke shi da karfi, inji rahoton jaridar Daily Trust.
Rundunar Yan sanda sun kama wani makiyayi da ake zargi da yanke hannun manomi a Bauchi
Da yake tabbatar da faruwar lamarin, babban sakataren yada labarai na gwamnan Kaduna, Mohammed Lawal Shehu, ya ce gwamnan ya umarci hukumomin tsaro da su bi bayan masu garkuwa da mutane tare da tabbatar da dawowar Yakasai lafiya.
Advertisements
