News
Iyayen Marayu A Jihar Kano Na Zanga-Zangar Tsadar Rayuwa
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI.
Tabarbarewar tattalin arziki da ya biyo bayan cire tallafin man fetur a kasar nan, ya tilastawa mata da Iyayen marayu a Kano gudanar da zanga-zangar lumana, inda suke bukatar hukumomi su dauki matakin magance matsalolin tsadar rayuwa.
Idan dai za a iya tunawa gwamnatin jihar Kano ta ce ta Siyo kayan abinci da ya kai naira biliyan 1 da dubu dari 6 domin rabawa talakawa kyauta, sai dai ba a fayyace ranafara rabon tallafin ba da kuma yadda za a raba.
Matan da suka fito daga Ja’een da makwaftan unguwanni dake kananan hukumomin Gwale da Kumbotso, ana tsaka da ruwan sama da yammacin ranar lahadi sun sha alwashin yin tattaki har zuwa gwamnatin Kano domin isar da kokensu.
Sun yanke shawarar cewa tallafin ba dole ba ne ya kasance kyauta, maimakon hakan a rage farashin abincin domin mutane masu yawa su samu damar amfana.
Shugabar masu zanga-zangar, Habiba Sulaiman Umar da Maryam Abdullahi Muhammad, sun ce yanayin tattalin arzikin ya gurgunta kananan sana’o’insu na cikin gida.
-
News6 days ago
ICPC Ta Yi Barazanar Daurin Shekaru 7 Ga Masu Yiwa Baki Rajistar NIN A Matsayin Yan Najeriya
-
News2 days ago
Jam’iyyar ADC Ta Yi Watsi Da Cire Ta Daga Rijista, Ta Sha Alwashin Kalubalantar Hukuncin Kotu
-
News7 days ago
Hayar Jirage Hadi Sirika Ya Dakko Daga Habasha Don Damfarar Yan Najeriya Da Sunan “Nigeria Air” — Shaida
