News
Kotu Ta Hana Hukumomin EFCC, CCB Da ICPC Binke Akan Muhyi Magaji Da Hukumarsa
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Wata Babbar Kotun Jihar Kano ta hana hukumar yaki da rashawa ta EFCC da hukumar ‘Da’ar ma’aikata da kuma hukumar yaki da rashawa ta ICPC shiga harkokin hukumar karbar korafe-korafe da yaki da rashawa ta jihar Kano.
Idan za’a iya tunawa EFCC da CCB sun rubuta wa hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta jihar Kano wasika inda suka bukaci gudanar da bincike akan ayyukanta da na shugabanta Barista Muhuyi Magaji Rimingado.
Chiyamomi A Jihar Ogun Sun Durkusa Sun Baiwa Gwamna Abiodun Hakuri
A wani umarni da ya bayar a ranar Litinin mai shari’a Farouk Lawan Adamu, ya ce umarnin ya hana EFCC da CCB da ICPC kamawa ko tsoma baki cikin harkokin duk wani ma’aikaci ko wani da ke karkashin ayyukan masu shigar da kara.
Daga nan ne kotun ta dage ci gaba da sauraron karar zuwa ranar 25 ga watan Satumba 2023.
-
News3 days ago
Wani Matashi Mai Shekaru 18 Ya Rasa Ransa Bayan Fadawa Cikin Ruwa A Kano
-
News3 days ago
Kaduna, Nasarawa, Zamfara Da Wasu Jihohi 10 Na Fuskantar Barazanar Ambaliyar Ruwa —NiMet
-
News4 days ago
Ba Za Mu Yi Wa Kowa Rangwame Ba A Wajan Yaƙi Da Sha Da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi Ba — Muhyi Magaji
