News
Tsadar rayuwa ta sanya wasu iyaye a kano sun ragewa ya’yansu ranakun zuwa makaranata.
DAGA FATIMA SULAIMAN SHU’AIBU
Al’ummar kasar nan dai na cigaba da nuna damuwa sakamakon kuncin rayuwar da suke ciki tun bayan da shugaban kasa bola Ahmad Tinubu ya janye tallafin man fetur.
wanda ya jefa da dama daga cikin al’umma cikin mawuyacin Hali.
tsadar man dai ta shafi fannoni da dama ciki harda kasuwanci,lafiya, ilimi,noma da dai sauransu.
Juyin Mulki 8 Da Sojoji Suka Yi A Shekaru 3 A Yammaci da Duma Tsakiyar Afirka.
wannan ne dalilin da yasanya iyayen dalibai a makaratun dake fadin jihar kano yanke shawarar rage wa yaransu ranakun zuwa makaranta.
Duk dai saboda matsalar tsadar ababen hawa da ya ninka, to sai dai kuma daukar wanna matakin da iyaye sukai mahukunta na ganin hakan na iya haifar da koma baya a karatun yayan nasu wanda hakan na iya kawo tazgaro a fannin ilimi.
Wanda a gefe guda kuma iyayen na ganin matakin da suka dauka shine mafita a garesu kasancewar komai na rayuwa yayi tsada baza su iya cigaba da biya wa yaran nasu kudin abin hawa ba kwanaki biyar a sati.
A zantawar jaridar Indaranka da wani magidanci. mai suna Malam Abubakar Abdullahi Dake zaune a unguwar hotoro a jahar kano ,wanda yake da yara 5 da suke zuwa makarantar sakandire ya bayyana cewa, tun bayan da aka janye tallafin man fetur da shugaban kasa yayi,abin hawa yayi tsada.
Wanda a da a kullum yakan bawa yaran nasa dari bakwai kudin mota. wanda a yanzu yakai naira 1500 yake basu.inda yace bazai iya cigaba da biyan wannan kudin a amatsayin kudin mota ba,don haka bashi da zabi sai dai ya rage musu ranakun zuwan nasu makaranta.
Magidancin ya kuma cigaba da cewa a babban abinda yake damunsu a yanzu shine batun tsadar kayan abincida da yayi tashin goron zabi.adon haka a yanzu bata kudin Mota suke ba domin kuwa Sai anci Abinci sannan za’a iya zuwa makaranta wannan ne dalilin su na daukar wannan mataki
Inda kuma yai fatan gwamnati harma da masu ruwa da tsaki zasuyi duba dangane da wannan batu wajan kawo musu dauki. sakamakakon halin da suke ciki a wannan lokaci.
Daukar wannan matakin da iyayen yaran sukayi masana na kallon hakan na iya zama babbar barazana ce ga ilimin yaran. sakamakon illar da hakan ka iya haifarwa ta fuskar ilimi.
