News
Ra’ayoyin Gwamnoni Ya Rabu Kan Lamarin Karin Albashi Na Wucin Gadi
DAGA MUHAMMAD ZAHRADDIN
Ra’ayoyin jahohin kasar sun rabu zuwa gida biyu kan yarjejeniyar da Gwamnatin Tarayya ta cimma da kungiyoyin kwadago na yin Karin naira dubu 35 ga ma’aikatan gwamnatin tarayya.
Yayin da wasu daga cikin jihohin suka ce za su karawa ma’aikatansu daidai da abunda gwamnatin tarayya ta tsara, wasu kuma sun ce tuni sun fara biyan ma’aikatansu Naira 10 kafin yarjejeniyar, a saboda haka ba su da wata alaka da matakin da gwamnatin tarayya ta dauka.
Shariar Gwamnan Kano: Gwamna Abba Kabir Ya ya garzaya Gaban Kotun Daukaka Kara
A yanzu haka gwamnatin jahar Enugu da Ondo sun amince su karawa ma’aikatansu naira dubu 35 a yayin da jihohin Kwara da Adamawa suka ce sun fara biyan ma’aikatansu karin naira dubu 10.
A jihohin Kebbi da Neja, gwamnatocin sun ce nan ba da jimawa ba za su zauna da ‘yan majalisar zartarwarsu domin tantance irin albashin da za a biya ma’aikatan.
Wani labarin kuma Shariar Gwamnan Kano: Gwamna Abba Kabir Ya ya garzaya Gaban Kotun Daukaka Kara
A yayin da ake cigaba da samun cikas wajen balaguro a filin jirgin sama na Murtala Muhammed dake Legas, biyo bayan komawar da kamfanonin jiragen sama na kasashen waje suka yi zuwa sabuwar tashar jiragen sama, gwamnatin tarayya ta gayyaci kamfanonin jiragen sama na kasashen waje zuwa wani taro a yau.
A sakamakon haka, kwamitin da ministan harkokin sufurin jiragen sama, Festus Keyamo ya kafa domin duba rudanin tafiye-tafiye a filin jirgin sama naMurtala Muhammad da kwamitin ministoci zai gana da masu ruwa da tsaki a domin nemo bakin zaren da warware matsalar.
Fasinjojin kasa da kasa da suka tashi daga Najeriya a ranakun Laraba da Alhamis sun makale a biranen Legas da Cairo da Doha da Landan, da sauran wurare bayan da madaurin kaya na jirgi ya lalace a sabon filin jirgin saman Murtala Muhammed da ke Legas, al’amarin da ya tilastawa kamfanonin jiragen sama jinkirtawa tare da soke tashin jirage.
Har yanzu zuwa karshen mako matsalar tafiye-tafiye na ci gaba da wanzuwa inda fasinjojin ke kwashe sa’o’i a kan layi domin tantance su ta hanyar binciken tsaro
