News
Majalisar wakilai ta ƙi yarda a yafe wa ɗalibai kuɗin WAEC da NECO da UTME da JAMB da su rubuta kyauta
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
A ranar Laraba ɗin nan ce Majalisar Tarayya ta yi fatali da roƙon neman amincewa da ƙudirin ɗaliban sakandare su rubuta jarawabar NECO, WAEC da JAMB kyauta a zangon 2023/2024.
An nemi a yi wa iyayen yara wannan afuwar biyan kuɗin jarabawar ce saboda a rage masu raɗaɗin tsadar rayuwar da ake fama da ita, tun bayan cire tallafin fetur.
Ɗan Majalisa Anamero Dekeri, ɗan APC daga Jihar Edo ne ys bijiro da roƙon, inda ya roƙi Majalisar Tarayya ta umarci Gwamnatin Tarayya ta biya wa kowane ɗalibi kuɗin jarabawar WAEC, NECO da UTME.
Sai dai kuma an yi fatali da buƙatar Ɗan Majalisar, bayan an yi doguwar mahawara a Zauren Majalisa.
Dekeri ya ce shi dai da zuciya ɗaya ya nemi a yi wa iyayen ɗalibai wannan sassauci, saboda irin halin ƙuncin da suka shiga, tun bayan cire tallafin fetur.
Ya ce kuɗin da talakawa ke kashewa kan fetur da tsadar zirga-zirga ya na yi wa ɗan abin da suke samu a yau da kullum babban giɓi.
Ya ce tunda Gwamnatin Tarayya ta tara rarar ɗimbin kuɗaɗe tun bayan cire tallafin fetur, to kamata ya yi ta yi wa iyayen ɗaliban da ke fita sakandare sassaucin su rubuta jarabawar 2023/2024 kyauta, ba tare da biyan ko sisi ba.
“A kullum tun da aka cire tallafin fetur, gwamnatin tarayya na ajiye tarar naira biliyan 17.2 a kowace rana.”
Kan haka ne ya yi roƙon cewa Ma’aikatar Ilmi ta Tarayya ya yi shelar yi wa iyayen ɗalibai sassaucin kada su biya kuɗaɗen NECO, WAEC da UTME.
An yi ta ja-in-ja, daga ƙarshe Kakakin Majalisar Tarayya, Abbas Tajudeen ya bada fili a yi zaɓe, inda waɗanda ba su so a yafe wa iyayen yara kuɗaɗen su ka yi nasara.
-
Opinion4 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News6 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News3 days ago
Gwamna Abba Ya Ayyana Murtala Sule Garo A Matsayin Wanda Zai Yi Masa Takarar Mataimakin Gwamna A Zaɓen 2027
