Connect with us

News

An Cire shugaban masu rinjaye na majalisar dokokin jihar Ribas Bayan Tashin Gobara

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN

 

Advertisement

Rikicin da ya barke a majalisar dokokin jihar Ribas ya dauki wani salo a ranar Litinin yayin da majalisar ta cire Edison Ehie a matsayin shugaban masu rinjaye.

Daily Trust ta rawaito cewa Edison Ehie babban mai goyon bayan Gwamna Similanayi Fubara ne. An ce ya ba da kunya ga yunkurin fara yunkurin tsige gwamnan.

Advertisement

Kwamitin Sulhu Na Majalisar Dinkin Duniya Zai Yi Zaman Gaggawa Akan Yakin Falasdinawa Da Isra’ila

Da yake sanar da tsige shugaban masu rinjaye a majalisar da ke zamanta a Fatakwal, babban birnin jihar, kakakin majalisar, Martins Amaehwule, ya ce an tsige shi ne saboda rashin halartar zaman majalisar.

Amaehwule yace kimanin yan majalisar 17 ne suka goyi bayan tsige dan majalisar.

Advertisement

A halin da ake ciki dai hukumomin tsaro sun mamaye harabar majalisar baki daya.

Wasu da ba a san ko su waye ba sun kona zauren Majalisar.

Advertisement

Rahotanni na nuni da cewa hakan yafaru ne da nufin dakile shirin tsige gwamnan, wanda rahotanni suka ce ya samu sabani da magabacinsa kuma ministan babban birnin tarayya (FCT), Nyesom Wike.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending