News
Kungiyar Kwadago Za Ta Shiga Yajin Aiki Kan Cin Zarafin Shugabanta, Joe Ajaero.
DAGA KABIRUBASIRU
Gamayyar ƙungiyoyin ƴan ƙwadago a Najeriya na NLC da TUC sun bayyana aniyarsu ta shiga yajin aikin gama-gari sanadiyyar kamawa da kuma dukan da aka yi wa shugaban ƙungiyar NLC, Joe Ajaero.
Ƙungiyar ta sanar da batun yajin aikin, wanda zai gudana a ranar Laraba ne a wata tattaunawa da manema labaru ranar Juma’a, a Abuja.
zaben Gwamnan Kano :Alkalai suna hukunta masu kada kuri’a kan kurakuran da INEC -Femi Falana
Shugabannin ƙungiyoyin sun bayyana cewa sun kuma bai wa Gwamnatin Tarayya sharuɗɗa shida da suke so a cika, ciki akwai sauke kwamishinan ƴan sanda na jihar Imo, da babban jami’in ƴan sanda na yankin da lamarin ya faru bisa zargin su da hannu a ‘cin zarafi da kuma wulaƙanta Mista Ajaero da sauran ƴaƴan ƙungiyar.”
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
