News
Yunƙurin juyin mulki: Ana musayar wuta a ƙasar Guinea
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Rahotanni daga ƙasar Guinea na nuni da cewa, ana zargin yunƙurin juyin mulki a ƙasar bayan da aka jiyo ƙazamar musayar wuta a Conakry, babban birnin ƙasar, a ranar Asabar.
Shaidu sun shaida wa Kamfanin Dillancin Labarai na AFP cewa, jami’an tsaro sun yi wa yankin ƙawanya, ba shiga ba fita.
Gwamanatin Tarayya Ta Ware Naira Biliyan 15 Domin Gyaran Gadar Jahar Legas
Wata majiya da aka sakaya sunanta ta ce, “Ana musayar wuta daga tsakanin ɓangarorin da lamarin ya shafa tare da harba makaman yaƙi a Kaloum.”
“Tun da asuba aka kulle garin, ba shiga, ba fita,” in ji wani ɗan kasuwa a yankin.
Guinea na ɗaya daga jerin ƙasashen da suka fuskanci juyin mulki tun 2020. Sauran ƙasashen sun haɗa da Mali, Burkina Faso, Nijar da kuma Gabon.
Shugaban sojojin juyin mulki a Guinea, Kanal Mamady Doumbouya, ya karɓe ragamar shugabancin ƙasar ne a ranar 11 ga Satumban 2021 bayan da ƙasar ta shafe shekara 11 kan turbar mulkin farar hula.
A wani labarin Gwamanatin Tarayya Ta Ware Naira Biliyan 15 Domin Gyaran Gadar Jahar Legas
Gwamnatin tarayya ta ce yanzu haka shirye-shirye sunyi nisa domin sauya akalar motoci har milyan 10 masu amfani da man fetir zuwa amfani da Gas nan da watanni 36 masu zuwa.
Karaminin ministan Mai, Ekperikpe Ekpo ne ya baiyana haka a yayin baje kolin mai da iskar gas na shekarar bana wanda ake gudanarwa a birnin Abu Dhabi na hadaddiyar daular larabawa.
A wata sanarwa da kakakinsa Louis Ibah ya fitar, ya baiyaan cewar a yanzu haka anyi kawance da kanfanoni masu zaman kansu domin kawo kayayyakin da za’a yi amfani dasu wajen sauya akalar motocin nan da watanni 9 masu zuwa.
Ya ce matakin wani yunkuri ne na inganta yin amfani da Gas a tsakanin motocin kasar a maimakon Man fetir da suka dogara dashi.
-
Opinion4 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News6 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News3 days ago
Gwamna Abba Ya Ayyana Murtala Sule Garo A Matsayin Wanda Zai Yi Masa Takarar Mataimakin Gwamna A Zaɓen 2027
