News
Gwamnatin Tarayya Za Ta Kirkiro Hukumar Kula Da Filaye
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Gwamnatin Tarayya ta sanar da ƙudirinta na kirkiro Hukumar Kula da Filaye ta Kasa.
Ministan Gidaje da Tsara Birane, Ahmed Dangari ne ya bayyana hakan, a taron zuba jari na ’yan Nijeriya mazauna kasashen ketare, karo na 6 da ya gudana a Abuja.
Yan Sandan Jihar Gombe sun kama wata mata bisa zargin ta da kashe mijinta ta da tabarya.
Ministan ya ce samar da sabuwar hukumar zai taimaka wajen kula da hakkin mallakar filaye a kasar nan.
Dangari ya kuma ce kirkiro hukumar na daga cikin sabbin manufofin Gwamnatin Tinubu na saita hanyoyin mallakar filaye.
“Rahoton kwamitin da shugaban kasa ya kafa kwanakin baya ya samar, kan sabbin dokokin mallakar filaye, karkashin Farfesa Peter Adeniyi, za a yi amfani da shi a sabuwar hukumar.
“Babu wata kasa da za ta samu ci gaba, ba tare da ta inganta dokokin kula da filayenta ba, ”in ji Dangari.
A wani labarin kuma Yan Sandan Jihar Gombe sun kama wata mata bisa zargin ta da kashe mijinta ta da tabarya.
Kamfanin dillancin labarai na AFP ya fitar da wasu hotuna da ke nuna jerin gwanon Falasɗinawa na barin Asibitin Al-Shifa a ƙafa.
Rahotonni sun ce ɗaruruwan mutane ne suka fice daga asibitin, wanda dakarun Isra’ila suka mamaye tsawon kwanaki.
Hotunan sun nuna maza, da mata, da yara na tafiya a kan titin da ɓaraguzai suka shafe yayin da wata motar rusau ta sojoji ke wucewa a bayansu.
Wakilin AFP ya ce daga cikin mutanen akwai marasa lafiya da waɗanda suka ji rauni yayin da suka kama hanyar zuwa kudancin Birnin Gaza daga arewaci.
Tun da fari, ma’aikatar lafiyar Gaza ta ce akwai marasa lafiya 120 da kuma wasu jarirai bakwaini da ba a san adadinsu ba da suka rage a asibitin.
Shugaban asibitin ya zargi Isra’ila da tilasta kwashe marasa lafiyar, amma dakarun sojan ƙasar na cewa wai sun taimaka ne wajen biyan buƙatar da shugaban ya nema.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
