Connect with us

News

Femi Falana ya ba Tinubu mako biyu ya biya diyya ga wadanda harin jirgin sama ya rutsa da su

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI

 

Femi Falana ya ba Tinubu mako biyu ya biya diyya ga wadanda harin jirgin sama ya rutsa da su

Babban lauya mai kare hakkin bil’adama, Femi Falana, SAN, ya ba gwamnatin tarayya wa’adin makonni biyu da ta biya diyya ga wadanda harin sojoji suka kai musu ta sama a cikin shekaru bakwai da suka gabata, ko kuma su fuskanci shari’a.

Gyara Bangaren Noma Zai Rage Rashin Aikin Yi Da Ta’addanci A Nijeriya- -Kashim Shettima

Babban lauyan ya yi wannan gargadin ne a wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi, inda ya kara da cewa za a gurfanar da gwamnati a gaban wata babbar kotun tarayya idan har ba a biya bukatar hakan ba.

DAILY POST ta bayar da rahoton cewa, sama da fararen hula 300 da suka hada da yara da mata ne suka mutu sakamakon tashin bama-bamai na bazata da sojojin Najeriya suka yi a shekarun baya.

Advertisement

A makon jiya ne aka kai harin bam mara matuki mara matuki a Tudun Biri da ke karamar hukumar Igabi a jihar Kaduna, lamarin da ya janyo cece-kuce a fadin kasar.

Akalla mazauna yankin 120 da ba su ji ba ba su gani ba, wadanda suke gudanar da bukukuwan addinin Musulunci ne aka kashe a wannan kazamin harin.

Kuma bayan faruwar wannan lamari mai ban tausayi, dukkanin Sanatoci 109 na Tarayyar Najeriya sun ba da gudummawar albashin watan Disamba ga wadanda harin bam ya rutsa da su.

A wani labarin kuma Gyara Bangaren Noma Zai Rage Rashin Aikin Yi Da Ta’addanci A Nijeriya- -Kashim Shettima

Gwamnatin tarayya ta ce yanzu haka shirye-shirye sunyi nisa domin sauya akalar motoci har milyan 10 masu amfani da man fetir zuwa amfani da Gas nan da watanni 36 masu zuwa.

Karaminin ministan Mai, Ekperikpe Ekpo ne ya baiyana haka a yayin baje kolin mai da iskar gas na shekarar bana wanda ake gudanarwa a birnin Abu Dhabi na hadaddiyar daular larabawa.

Advertisement

A wata sanarwa da kakakinsa Louis Ibah ya fitar, ya baiyaan cewar a yanzu haka anyi kawance da kanfanoni masu zaman kansu domin kawo kayayyakin da za’a yi amfani dasu wajen sauya akalar motocin nan da watanni 9 masu zuwa.

Ya ce matakin wani yunkuri ne na inganta yin amfani da Gas a tsakanin motocin kasar a maimakon Man fetir da suka dogara dashi.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending