News
Majalisar Dokokin Sokoto Ta Amince Da Bukatar Gwamna Aliyu Na Kafa Jami’an Tsaron Jiha
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
A ranar Laraba Majalisar Dokokin Jihar Sakkwato ta amince da kudirin Gwamna Ahmed Aliyu na kafa rundunar samar da zaman lafiya a jihar.
Wannan amincewar ta biyo bayan nazarin rahoton da kwamitocin majalisar hadin guiwa kan ayyuka na musamman da harkokin tsaro da shari’a da kwamitin kare hakkin bil’adama suka yi.
Yansanda Sun Kama Wasu Mutane 5 Kan Mallakar Bindigu Kirar AK-47 Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Jihar Katsina
Shugaban Kwamitin, Alhaji Nasiru Adamu (PDP-Goronyo), ya ruwaito cewa, an binciki kudurin dokar, wanda ya samar da shawarwari 28.
“Wadannan shawarwarin sun hada da sake fasalin dokar zuwa, ‘Kudirin dokar kafa hukumar tsaro ta al’ummar jihar Sakkwato, da samar da zaman lafiya da tsaron lafiyar jama’a da dukiyoyinsu, da kuma gaggauta daukar matakan gaggawa,” in ji shi. .
Adamu ya kara da cewa akwai bukatar a samar da sabon sashe dangane da adadin jami’an da ke aiki da kuma gyara kura-kuran rubutu, fasaha da rubutawa daga sashin kula da shari’a.
Shugaban majalisar Alhaji Tukur Bala ya gabatar da rahoton domin tantancewa kuma ‘yan majalisar sun amince da bukatar ta hanyar kada kuri’a.
-
News5 days ago
Dakarun Soji Cafke Wani Shugaban ’Yan Ta’adda a Kaduna, Sun Kwato Harsasai 300
-
News6 days ago
Dan Takarar Gwamnan Kano a Jam’iyyar AP Ya Yi Allah-Wadai Da Kisan Gillar Da Aka Yi Wa Dan-Shagamu
-
News20 hours ago
Rundunar ‘Yansanda Ta Yi Gargaɗi Gam Da Yiwuwar Kai Hare-hare Makarantu Da Wuraren Ibada
