News
EFCC Ta binciken wasu Kamfani 52 Kan Mu’amalar Ta’addanci a karkashin jagorancin tsohon gwamnan babban bankin kasa, Godwin Emefiele.
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa, EFCC, ta na binciken wasu kamfanoni 52 kan hada-hadar kudaden waje da babban bankin Najeriya CBN.
Hukumar ta EFCC na binciken kudaden da aka ware wa kamfanoni 52 karkashin jagorancin tsohon gwamnan babban bankin kasa, Godwin Emefiele.
Rundunar Ƴan sanda sun kama likitan da ya yi wa wata budurwa allurar zubar da ciki ta mutu a Kano
Hukumar ta rubuta wa kamfanoni daban-daban suna neman takardu kan hada-hadar cinikinsu a cikin shekaru 10 da suka gabata, kamar yanda Jaridar TheCable ta ruwaito.
Wasu daga cikin kamfanonin da ake binciken sun hada da Dangote Group, BUA Group da kuma Flour Mills – amma duk sun musanta aikata ba daidai ba a sadarwar su da EFCC.
A baya SaharaReporters ta rawaito cewa jami’an hukumar EFCC sun gudanar da bincike a babban ofishin kamfanin Dangote a Legas.
Rahotanni sun bayyana cewa jami’an na EFCC sun gudanar da bincike kan kudaden da aka ware wa kamfanin a lokacin Emefiele a matsayin Gwamnan CBN.
Kakakin EFCC, Dele Oyewale, shi ma ya tabbatar da faruwar lamarin.
Rahotanni na nuni da cewa kamfanin Dangote ya ce a shirye yake yayu bayanin duk wani abu da ya shafi kasuwancin ta na forex domin ba ta karya wata doka ba.
Cikakkun bayanai na binciken hukumar EFCC har yanzu ba su da kyau amma da alama bincike ne akan manyan kamfanonin da suka samu kudaden shiga daga CBN a karkashin Emefiele.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
