Connect with us

Sports

Dalilin da ya sa AS Roma ta zabga wa Jose Mourinho takardar sallama

Published

on

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN

 

Advertisement

Jose Mourinho ya fuskanci sallamarsa ta shida, a wannan karon da kungiyar kwallon kafa na AS Roma bayan kusan shekaru uku a kungiyar.

Sanarwar da AS Roma ta fitar ta ce” Aiki tsakanin ta da Mourinho ya kare kwatakwata.

Advertisement

Sai Kun Yi Haƙuri, Amma Sai Gwamnati Ta Ɗauki Matakai Masu Tsauri – Buhari

Sanarwar ta ci gaba da cewa: “Muna so mu gode wa José a madadin mu duka a AS Roma saboda da kokarinsa tun zuwansa kulob din,” in ji Dan da Ryan Friedkin.

Muna yi wa José da mataimakansa fatan alheri a ayyukansu na gaba.”

Advertisement

Wannan shi ne karo na shida da kociyan mai shekaru 60 ke barin kulob, inda a baya ya fice daga Chelsea a 2007 da 2015, Real Madrid a 2013, Manchester United a 2018, da Tottenham a 2021.

An bayyana shi a matsayin kocin kungiyar na 60 a watan Mayun 2021, zaman Mourinho a Roma ya hada da lashe gasar League a kakar wasa ta 2021/22 da kaiwa wasan karshe na gasar Europa a Budapest a watan Mayun da ya gabata.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending