Sports
Najeriya ta yi wajerod da Afirka ta Kudu a bugun fenareti, kuma ta kai wasan ƙarshe.
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
Najeriya ta samu nasarar zuwa wasan ƙarshe a gasar cin koin ƙwallon ƙafa na nahiyar Afirka, 2023 da ke gudana a Ivory Coast.
Najeriyar ta kai wasan na ƙarshe ne bayan ta doke Afirka ta Kudu a bugun fanareti da ci 4-2.
A yanzu Najeriya za ta kara da duk ƙasar da ta yi nasara a karawar da ake yi yanzu haka tsakanin mai masaukin baƙi Cote d’Ivore da Jamhuriyar Demokuradiyyar Congo.
An je bugun fanareti ne a wasan Najeriya da Afirka ta Kudu ne bayan kwashe minti 120 ana fafata wasa ba tare da an samu ƙasar da ta zura ƙwallaye mafi yawa ba.
Inda aka tashi wasan Najeriya na da ƙwallo ɗaya, Afirka ta Kudu ma tana da ƙwallo ɗaya.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
