Connect with us

News

MTN ya nemi afuwar abokan hulɗarsa kan ɗaukewar sabis a Najeriya

Published

on

MTN

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN

Kamfanin sadarwa na MTN a Najeriya ya nemi afuwar aboka huldarsa sakamakon matsalar ɗaukewar sabis da kamfanin ya fuskanta a faɗin ƙasar.

Cire tallafin fetur ya zama ciwon ido, sai haƙuri –Shugaba Tinubu

Tun da tsakar ranar Laraba ne dai masu amfani da layin MTN suka fara fuskantar matsalar ɗaukewar sabis a layukansu.

To sai dai kamfanin cikin wata sanarwa da ya fitar a shafinsa na X, ya ce hakan ya faru ne sakamakon yankewar wasu wayoyin sadarwar kamfanin, lamarin ya ya shafi kira da kuma fannin intanet a layin.

Kamfanin ya kuma ce injiniyoyinsa na aiki domin shawo kan matsalar, inda ya ce sannu a hankali sabis ɗin ya fara dawowa a wasu yankuna.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending