News
Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Tinubu tsige wasu manyan jami’ansa
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Majalisar Dattawa ta amince da buƙatar da Shugaba Bola Ahmad Tinubu ya gabatar mata ta neman tsige Mataimakin Babban Jami’in Hukumar FCCPC, Barrister Babatunde Irukera.
Wasiƙar da Tinubun ya aike wa Majalisar wadda Shugaban Majalisar ya karanto ta yayin zaman Majalisar a ranar Laraba, ta nuna Tinubu ya buƙaci tsige Irukera ne saboda rashin kataɓus.
Wasu ƴan bindiga ɗauke da makamai sun yi awon gaba da wasu masallata cikin masallacin a Zamfara.
Dokar FCCPC ta tanadi cewa, sai da sahalewar Majalisar Dattawa kafin Shugaban Ƙasa zai iya tsige Mataimakin Babban Jami’in Hukumar.
Sanarwar da ta nuna tsige Irukera ta sake nuni da yadda Tinubu ya tsige Babban Daraktan hukumar Bureau of Public Enterprises (BPE), Alex Okoh, tare da sanar da waɗanda za su maye guraben waɗanda tsigewar ta shafa.
Bayan tafka zazzafar muhawara kan wasiƙar a zauren Majalisar, daga bisani Shugaban Majalisar, Sanata Apkabio ya ba da damar kaɗa ƙuri’ar jin ra’ayi wanda a ƙarshe waɗanda suka goyi bayan wasiƙar suka yi rinjaye.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
