News
Wasu ƴan bindiga ɗauke da makamai sun yi awon gaba da wasu masallata cikin masallacin a Zamfara.
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Wasu ƴan bindiga ɗauke da makamai sun yi awon gaba da wasu masallata a ɗaya daga cikin masallacin da ke garin Tsafe hedikwatar ƙaramar hukumar Tsafe a jihar Zamfara.
Wani ɗan yankin mai suna Garba ya bayyana cewa ƴan bindigar sun mamaye masallacin ne da misalin karfe 5 na safiyar ranar Alhamis a lokacin da mutanen ke shirin fara Sallar Asuba.
Kada ku rasa wannan damar, saka hannun jari Yanzu A company BAHAL DATA Ga dama ta samu
Garba ya ce, “Yau alhamis muna shirin tada sallar asuba, kwatsam sai ga yan bindiga sun dira masallaci inda suka umurci duk jama’an ciki su biyo su inda Ni na yi nasarar ɓoyewa ba su ganni ba.”
Ya ƙara da cewa saboda kar a ji karar abin bawan su sai suka ajiye Baburan su can nesa.
A ƙalla mutane 30 ne aka yi awon gaba da su.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
