News
Yan sanda sun kama shugaban makarantar bisa zargin yi wa wata daliba bulala da kuma raunata
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Rundunar ‘yan sanda ta cafke wani shugabar makarantar sakandare a unguwar Igando da ke Legas bisa zargin yi wa wata daliba bulala da kuma raunata a jikinta.
Kakakin rundunar ‘yan sandan, SP Benjamin Hundeyin, ne ya shaidawa Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya NAN a ranar Asabar cewa rundunar ‘yan sandan Igando ta dauke shugaban makarantar a ranar Juma’a domin yi masa tambayoyi.
Hada Layuka Da NIN: Kamfanin Sadarwa Na MTN Ya Kulle Layukan Mutum Miliyan 4.2 A Nijeriya
Hundeyin ya ce ma’aikatar ilimi ta jihar Legas ita ma ta sa baki a lamarin, da nufin a binciki shugaban makarantar, tare da gurfanar da shi gaban kuliya, idan aka same shi da laifi.
Daily News24 ta ruwaito cewa wani faifan bidiyo ya bayyana a yanar gizo wanda ke nuna wata daliba da alamomi a jikinta, wanda ake zargin an yi mata bulala.
Hakan ya sa kwamishinan ‘yan sanda na jihar Legas, kwamishinan ilimi, da kwamishinan matasa da ci gaban al’umma su sa baki a kan lamarin.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
