News
‘Yan bindiga a Bauchi sun kashe basarake sa’o’i 24 bayan sun yi garkuwa da shi
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
‘Yan bindiga a Jihar Bauchi sun kashe Dagacin ƙauyen Riruwai, Alhaji Garba Bafamasi, da ke yankin Ƙaramar Hukumar Toro a jihar.
MANHAJA ta kalato cewar, ‘yan ta’addan sun kashe basaraken ne sa’o’i 24 bayan da suka yi garkuwa da shi.
Rahotanni sun ce a ranar Juma’a, 15 ga Maris, ‘yan bindigar suka dira fadar Alhaji Badamasi inda suka razanar da jama’ar yankin da harbin bindiga kafin daga bisani suka yi awon gaba da shi.
Majaiyarmu ta ce, ‘yan bindigar ba su damu da kiran ‘yan basaraken don neman fansa ba, lamarin da ya sa aka kasa gane dalilin da ya sa suka aikata masa haka.
Bayan kwana guda da yin garkuwa da marigayin sai aka tsinci gawarsa a gefen gari kusa da ƙauyen.
An gano gangar jikin ne a lokacin da jama’ar kauyen suka baza neman basaraken a daji.
-
News19 hours ago
Jam’iyyar Labour Party Ta Yi Alkawarin Kafa Hukumar Kula Da Hayar Gidaje A Kano
-
News3 days ago
Shettima @60: Haƙurinsa, Biyayyarsa Sun Taimaka Wajen Ciyar Da Manufofin Shugaba Tinubu Gaba — Kwankwaso
-
News6 days ago
KANO:’Yan Mata Uku ’Yan Gida Ɗaya Sun Mutu A Kifewar kwale-kwale A Tiga
