Connect with us

News

‘Yan bindiga a Bauchi sun kashe basarake sa’o’i 24 bayan sun yi garkuwa da shi

Published

on

Advertisements
ads

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

‘Yan bindiga a Jihar Bauchi sun kashe Dagacin ƙauyen Riruwai, Alhaji Garba Bafamasi, da ke yankin Ƙaramar Hukumar Toro a jihar.

MANHAJA ta kalato cewar, ‘yan ta’addan sun kashe basaraken ne sa’o’i 24 bayan da suka yi garkuwa da shi.

Saraki  Ya Kai Ziyarar Gani Da Ido, Domin Ganin Yadda Ake Tantance Ɗalibai 100 Da Gidauniyarsa Ta Ɗauki Nauyin Karatunsu 

Rahotanni sun ce a ranar Juma’a, 15 ga Maris, ‘yan bindigar suka dira fadar Alhaji Badamasi inda suka razanar da jama’ar yankin da harbin bindiga kafin daga bisani suka yi awon gaba da shi.

Majaiyarmu ta ce, ‘yan bindigar ba su damu da kiran ‘yan basaraken don neman fansa ba, lamarin da ya sa aka kasa gane dalilin da ya sa suka aikata masa haka.

Bayan kwana guda da yin garkuwa da marigayin sai aka tsinci gawarsa a gefen gari kusa da ƙauyen.

Advertisement

An gano gangar jikin ne a lokacin da jama’ar kauyen suka baza neman basaraken a daji.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending