Connect with us

Business

Muna sane da tsare ɗanƙasarmu ma’aikacin Binance a Najeriya – Amurka

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN

Amurka ta ce tana da masaniya a kan rahotannin tsare ɗanƙasarta a Abuja, babban birnin Najeriya.

Kungiyar Kare Hakkin Dan Adam Ta IHR Ta Bukaci Majalisa Ta Sasanta Da Abdul Ningi

A watan da ya gabata ne aka kama shugaban kamfanin Binance, Tigran Gambaryan tare da abokin aikinsa, Nadeem Anjarwalla, wanda ke da fasfon Birtaniya da Kenya a wani ɓangare na binciken kaucewa biyan haraji da gwamnatin Najeriya ke yi wa kamfanin na kuɗin kirifto.

Mai magana da yawun ofishin jakadancin Amurka a Najeriya, ya shaida wa BBC cewa, “A duk lokacin da aka samu wata matsala ta tsare ɗanƙasarsu a wata ƙasa, to ofishin jakadancin da ke ƙasar na yin duk mai yiwuwa wajen bayar da taimakon da ya dace.”

Ofishin jakadancin ya ƙi bayar da cikakken bayanai game da tsare ɗanƙasar, yana mai cewa saboda dalilai na sirri.

Advertisement

Yanzu haka Nadeem Anjarwalla, ba ya hannun Najeriya bayan da mahukuntan ƙasar suka tabbatar da cewa ya tsere, to amma wata majiya daga makusantansa ta ce ya bar Najeriya ne ta hanyar da ta dace.

Mahukuntan Najeriya dai sun ce suna aiki da jami’an tsaro don samar da takardar sammaci ga Mr Anjarwalla.

A ɓangare guda kuma, mahukuntan Najeriya sun maka kamfanin a gaban kotu inda suka shigar da tuhume-tuhume da suka shafi ƙin biyan haraji.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending