Connect with us

News

Cikakken bayanin yadda Shugaba Tinubu ya kafa Majalisar Havaka Tattalin Arzikin Nijeriya

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI TUKUNTAWA 

A wani muhimmin mataki na ƙarfafa tsarin tafiyar da tattalin arzikin qasa da tabbatar da tsayayyen tsare-tsare da aiwatar da tattalin arzikin ƙasa cikin aminci, Shugaban Nijeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya amince da ya kafa Kwamitin Kula da Tattalin Arzikin Ƙasa na Shugaban Ƙasa (PECC) da kuma samar da Ƙungiyar Kula da Tattalin Arziki ta Gaggawa (EET).

Advertisement

A cewar wata sanarwa mai ɗauke da sa hannun Ajuri Ngelale, mai ba shugaban ƙasa shawara na musamman kan kafafen yaɗa labarai da wayar da kan jama’a, kwamitin kula da tattalin arzikin shugaban ƙasa (PECC) ya ƙunshi fitattun shugabanni da manyan jami’an gwamnati da suka haɗa da:

An gyara tashoshin samar da wutar lantarki da suka daina aiki a Najeriya

(1) Shugaban Tarayyar Nijeriya – Shugaban Hukumar PECC

Advertisement

(2) Mataimakin Shugaban Tarayyar Nijeriya – Mataimakin Shugaban PECC da NEC

(3) Shugaban Majalisar Dattawan Nijeriya

Advertisement

(4) Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Nijeriya

(5) Ministan tattalin arziki da kuma ministan kuɗi

Advertisement

(6) Gwamnan Babban Bankin Nijeriya

(7) Ministan Noma da Tsaron Abinci

Advertisement

(8) Ministan sufurin jiragen sama da raya sararin samaniya

(9) Ministan Kasafin Kuɗi da Tsare Tattalin Arziki

Advertisement

(10) Ministan Sadarwa, Ƙirƙira da Tattalin Arziki na Dijital

(11) Ministan Masana’antu, Ciniki da Zuba Jari

Advertisement

(12) Ministan Qwadago da Samar Da Ayyukan yi

(13) Ministan Ruwa da Tattalin Arziki

Advertisement

(14) Ministan Wutar Lantarki

(15) Ƙaramin Ministan Albarkatun Man Fetur

Advertisement

(16) Ƙaramin Ministan Gas

(17) Ministan Sufuri

Advertisement

(18) Ministan Ayyuka

Kwamitin na PECC zai kuma ƙunshi manyan mambobi na kamfanoni masu zaman kansu, tare da sauran mambobi da za su yi aiki na tsawon shekara guda, bisa ga umarnin shugaban ƙasa:

Advertisement

(1) Alhaji Aliko Dangote

(2) Mr. Tony Elumelu

Advertisement

(3) Alhaji Abdulsamad Rabiu

(4) Malama Amina Maina

Advertisement

(5) Malam Begun Ajayi-Kadir

(6) Madam Funke Okpeke

Advertisement

(7) Dr. Doyin Salami

(8) Mr. Patrick Okigbo

Advertisement

(9) Malam Kola Adesina

(10) Mr. Segun Agbaje

Advertisement

(11) Malam Chidi Ajaere

(12) Malam Abdulkadir Aliu

Advertisement

(13) Malam Rasheed Sarumi

 

Advertisement

Bugu da ƙari, a cikin ƙudirinsa na magance matsalolin tattalin arziki cikin hazari da kuma tabbatar da ingantaccen aiwatar da dabarun tattalin arziki, Shugaba Bola Tinubu ya kafa Ƙungiyar Kula da Tattalin Arziki ta Gaggawa (EET) tare da umarni aiwatar da tsarin tattalin arziki cikin gaggawa.

 

Advertisement

Ƙungiyar ta ƙunshi manyan jami’an gwamnati da shugabannin masana’antu don haɓaka tsarin haɗin gwiwar shugaban aasa don samun ƙarfin tattalin arziki da cigaba. A yanzu an wajabta wa EET gabatar da wani cikakken tsari tattalin arziki na shekarar 2024 ga kwamitin PECC, wanda ya ƙunshi watanni shida masu zuwa, don aiwatarwa cikin gaggawa cikin makonni biyu da ƙaddamar da ita. EET za ta haɗu sau biyu a mako kuma ta ƙunshi mambobi kamar:

 

Advertisement

(1) Ministan Tattalin Arziki kuma Ministan Kuɗi (Shugaban EET)

(2) Ministan Kasafin Kuɗi da Tsare Tattalin Arziki

Advertisement

(3) Ministan Wutar Lantarki

(4) Ministan Noma da Tsaron Abinci

Advertisement

(5) Ministan Lafiya da Jin Daɗin Jama’a

(6) Ministan Masana’antu, Ciniki da Zuba Jari

Advertisement

(7) Gwamnan Babban Bankin Nijeriya

(8) Mai Ba Ƙasa Shawara Kan Harkokin Tsaro

Advertisement

(9) Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Nijeriya

(10) Gwamnan jihar Anambra

Advertisement

(11) Gwamnan jihar Ogun

(12) Gwamnan Jihar Neja

Advertisement

(13) Shugaban Ma’aikatar Harajin Cikin Gida ta Tarayya

(14) Darakta-Janar, Ofishin Kasafin Kuɗi na Tarayya

Advertisement

(15) Shugaban Kamfanin NNPC

(16) Shugaban Ƙungiyar Tattalin Arzikin Nijeriya

Advertisement

(17) Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara Kan Makamashi

(18) Dr. Bismarck Rewane, Masanin Tattalin Arziki

Advertisement

(19) Dr. Suleyman Ndanusa, masanin tattalin arziki

 

Advertisement

Tawagar Gudanar da Tattalin Arziki, wacce aka kafa a watan Oktoba 2023, kuma Ministan Kula da Tattalin Arziki da kuma Ministan Kuɗi ke jagoranta, tana aiki a matsayin ƙungiya a ƙarƙashin Kwamitin Gudanar da Tattalin Arziƙi na Shugaban Ƙasa (PECC), suna taka muhimmiyar rawa a tsarin tafiyar da tattalin arzikin da aka kafa. EMT a al’adantu wajen ƙirƙirar hanyoyin havaka tattalin arziki. EMT ta ƙunshi jami’ai kamar:

 

Advertisement

(1) Ministan Tattalin Arziki da Ministan Kudi (EMT Chairman)

(2) Gwamnan Babban Bankin Nijeriya

Advertisement

(3) Ministan Kasafin Kuɗi da Tsare Tattalin Arziki

(4) Ministan Masana’antu, Kasuwanci da Zuba Jari

Advertisement

(5) Ministan Sadarwa, Ƙirƙira da Tattalin Arziki na Dijital

(6) Ministan Ayyuka

Advertisement

(7) Ministan Kwadago da Aiki

(8) Ministan Noma da Tsaron Abinci

Advertisement

(9) Ƙaramin Ministan Albarkatun Man Fetur

(10) Ƙaramin Ministan Gas

Advertisement

(11) Ministan wutar lantarki

(12) Ministan Sufuri

Advertisement

(13) Ministan sufurin jiragen sama da raya sararin samaniya

(14) Ministan Ruwa da Tattalin Arziki

Advertisement

 

Shugaban EMT na iya, kamar yadda ake buƙata, ya kira kowane Ministan Tarayya ko Shugaban Hukumar don yi wa EMT bayani kan muhimman shirye-shirye da ci gaban da suka shafi tattalin arziki.

Advertisement

 

Ƙirƙirar kafa PECC da Shugaban Ƙasa ya yi a ƙarƙashin shugabancinsa, tare da ƙirƙirar EET, wanda shugaban EMT ya jagoranta, da kuma EMT kanta, alama ce ta haɗaɗɗiyar dabarun da ke nufin inganta tsarin tafiyar da tattalin arzikin Nijeriya don inganta ƙasar.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending