Connect with us

News

Rundunar Ƴan Sanda Ta  Kama Mutum 4 Bisa Yinkurin Ƙona Sansanin Ƴan Gudun Hijira

Published

on

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN

Rundunar ƴan sandan jihar Borno ta gurfanar da wasu mutane huɗu da ake zargi da yunƙurin cinna wuta a sansanin yan gudun hijira da ke Mafa a jihar Borno.

Jaridar Punch ta ruwaito cewa sunayen waɗanda ake zargin su ne Malum Usman mai shekaru 16; Bulama Bukar, 14; da Rawa Usman, 11; wanda ake zargin wani Babagana Umar mai shekaru 40 shi ne ya ɗauki nauyinsu.

Liverpool Ta Dare Saman Teburin Gasar Premier

An sami rahoton ne a lokacin da wata kungiyar mafarauta a Mafa ta kai rahoto ga ƴan sanda cewa an kama waɗanda ake zargin da ashana a lokacin da suke kokarin bankawa wani gida wuta a sansanin ƴan gudun hijira a ranar 24 ga watan Maris, 2024, da misalin karfe 10:30 na safe.

ASP Kenneth Nahum Daso, ya ce sun gano cewar Babagana Umar ya ce zai biya waɗannan yara kuɗi Naira 10,000.Sai dai wanda ake zargin ya musanta.Inda yanzu haka ƴan Sanda na gudanar da bincike.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending