News
Hukumar EFCC Ta Je Kama Tsohon Gwamnan Kogi Yahaya Bello
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Jami’an Hukumar Yaki da masu karya tattalin arziki (EFCC) sun kai samame gidan tsohon gwamnan jihar Kogi Bello da ke Abuja.
Wakilin jaridar Daily trust ya is layin Benghazi a unguwar Wuse da gidan na Yahaya Bello yake, inda ya ga jami’an na EFCC.
Yadda Sauraron Ƙarar Da Gwamnatin Kano Ta Shigar Kan Ganduje Ta Kasance.
Wani babban jami’in EFCC da ya bukaci wakilin namu ya sakaya sunansa ya tabbatar cewa sun kai samamen ne da nufin kama da Yahaya Bello.
Sai da kuma jami’in ya ki amsa tambayar wakilin namu game da zargin da hukumar ke wa tsohon gwamnan.
Ana dai tunanin samamen na da alaƙa da badaƙalar Naira biliyan 84 na jihar Kogi a zamanin mulkin Yahaya Bello da EFCC ke bincike a kai.
Kokarin wakilinmu na samun karin bayani daga kakakin EFCC, ya ci tura.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
