News
Ɗan Ganduje Ya Kai Wa Muhuyi Ziyarar Ƙarfafa Gwiwa Kan Yaƙi Da Cin Hanci
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Abdulazeez Ganduje, wanda shi ne babban ɗan tshohon gwamnan jihar Kano Abdullahi Ganduje, ya kai wa shugaban hukumar yaƙi da cin hanci Muhuyi Magaji Rimingado, ziyara a yau Laraba 17 ga watan 4, 2024.
Majiya mai karfi da tabbatarwa da jaridar DAILY NIGERIAN Hausa cewa Abdulazeez ya goyi bayan kai mahaifinsa gaban kuliya bisa zargin cin hanci da rashawa.
Kuma majiyar ta ce ya nuna ɓacin ransa bisa cire sunansa da mahaifinsa ya yi ba da izininsa ba daga cikin daraftocin ɗaya daga cikin kamfanunnukan da a ke zargi da handame kuɗin al’umma.
Advertisements
