News
Kotu Ta Ɗaura Tarar Naira Miliyan 300 Ga ‘Yan Sandan Da Suka Farwa Ƴan Shi’a
DAGA NUSAIBA ABDULLAHI TUKUNTAWA
Wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Kaduna ta umurci hukumar ƴan sanda da su biya zunzurutun kuɗi har Naira miliyan 300 ga iyayen ƴan Shi’a uku da ake zargin jami’anta sun kashe a lokacin da suke gudanar da muzaharar shekarar 2022 a Zariya.
Wiki Time ta ruwaito cewa Mai shari’a Hawa Buhari, a cikin hukuncin da ta yanke, ta ce “haƙƙoƙin na su an tanada shi a cikin sashe na 33, 38, 39, 40, 42 da 46 na kundin tsarin mulkin 1999 Umarni na 2, Dokokin 1, 2, 3, 4, 11 da 12 na Dokokin Haƙƙin Mahimmanci (Tasirin Tilasta) Dokokin 2009; Ana aiwatar da doka ta 4, 8, 10, 11 da 12 na Yarjejeniya Ta Afirka ta 2004 game da ƴancin ɗan adam da jama’a.”
Zafin Rana, Tsananin Rashin Ruwan Sha, Rashi da Tsadar Man Fetur, mutanen Najeriya na neman agaji
Mai shari’ar ta jaddada cewar adadin Naira miliyan 100 ya zama tilas a biya duka iyayen uku, inda za a biya jimillar Naira miliyan 300 kenan, a matsayin diyya, kuma za a rika samun ribar kashi 10 cikin 100 a duk shekara har sai an gama biyan kudaden.
Mai shari’a Buhari, a hukuncin da ta yanke a ranar 22 ga Afrilu, 2024, wanda aka fitarwa da manema labarai kwarin a ranar Lahadi a Abuja.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
