News
Majalisar Dattawa Ta Fara Yunkurin Ragewa Karfin Fada Ajin Da CBN Ke Da Shi
DAGA NUSAIBA ABDULLAHI TUKUNTAWA
Majalisar dattawan Najeriya ta fara mahawara domin rage karfin fada ajin da Babban bankin kasar na CBN ke da shi a kan batutuwan da suka shafi tattalin arzikin kasa.
A karkashin sabon kudirin da ake mahawara a kai, Babban bankin zai ci gaba da shugabancin batutuwan da suka shafi hada hadar kudade na kasa, yayin da wani sabon kwamiti a karkashin ministan kudi zai karbe ikon aiwatar da manufofin kudaden.
Wannan kudiri na zuwa ne a daidai lokacin da hauhawan farashin kayayaki a Najeriya ya yi tashin da ba’a taba ganin irinsa ba a cikin shekaru 28, inda ya kai kashi 33.69 a watan Afrilun da ya gabata kamar yanda Radiyon Faransa ta ruwaito
Advertisements
