News
Gwamnatin tarayya ta gayyaci Kungiyoyin Kwadago Domin Kawo Karshen Yajin Aiki
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Sa’o’i 16 da fara yajin aikin gama-gari a fadin kasar nan, gwamnatin tarayya ta gayyaci tagwayen kungiyoyin kwadagon domin tattaunawa kan kawo karshen yajin aikin.
A kokarin da take yi na kawo karshen yajin aikin da aka yi a daren Lahadin da ta gabata, gwamnatin tarayya ta hannun hukumar biyan albashi ta kasa ta mika goron gayyata ga shugabannin kungiyoyin kwadagon Najeriya NLC da TUC. ).
Rahoton ya ce akwai cikakken bin umarnin ma’aikata da Ma’aikatu, da Hukumomi, cibiyoyin kudi, a asibitocin gwamnati, da bangaren wutar lantarki da dai sauransu.
Da aka tuntuba dan jin ko kungiyoyin kwadagon za su mutunta gayyatar, wata majiya ta ce za a yanke hukuncin ne a karshen taron majalisar zartarwa ta kasa da kungiyoyin za su yi a yau.
Hukumar Labour tace ba ta rufe kofarta kan batun mafi karancin albashi ba Kuma zamu, ci gaba za mu auna gayyata, don haka ba za mu bata lokacinmu ba.
“Bukatunmu a bayyane suke a baiwa ‘yan Najeriya mafi karancin albashi”.
SOURCE THE HISTORICAL NIGERIA
