Connect with us

News

Aikin Hajji: Wata Hajiya daga Najeriya ta kashe kan ta a Madina

Published

on

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN 

Wasu maniyyata guda biyu ƴan asalin jihar Kwara da ke aiwatar da aikin Hajjin bana a ƙasar Saudiyya daga jihar Kwara; Salihu Mohammed da Hawawu Mohammed, sun rasu a birnin Madina.

Advertisement

Sakataren zartarwa na Hukumar Alhazai ta Jihar Kwara, AbdulSalam AbdulKabir, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi.

Aikin Hajji: Karin Wani Mahajjacin Daga Jihar Kebbi Ya Rasu A Makkah

A cewar sa, yayin da Salihu Mohammed ya rasu a sashin kula da marasa lafiya na musamman na asibitin gwamnati da ke Madina bayan ya fara jinya cikin ƙanƙanin lokaci.

Advertisement

Wikki Times ta ruwaito cewa Hauwa’u Mohammed ta rasu, bayan abin da hukumomin ƙasar Saudiyya suka gudanar da bincike suka gano cewa ta kashe kanta ne, ta hanyar faɗowa, da gangan, daga saman benen masaukinta da ke Madina.

Hukumomin Saudiyya da na jihar Kwara sun bayyana faruwar lamarin a matsayin abin takaici gami da bakin ciki tare da mika sakon ta’aziyya ga iyalan mamatan.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending