News
DA DUMI-DUMI: ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari A Kauyen Sokoto, Sun Kashe Mutum 10, Sun Sace Da Dama A Ranar Sallah
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Wasu ‘yan ta’adda dauke da makamai sun kai wani mummunan hari a kauyen Dudun Doki da ke karamar hukumar Gwadabawa ta jihar Sakkwato a safiyar Ranar Lahadi.
DA DUMI-DUMI: Jaridar Inda Ranka Tana Taya Al’ummar Musulmi Murnar Bikin Babbar Sallah
Maharan sun kai farmaki kauyen ne da misalin karfe 1:30 na safe, inda suka kashe sama da mutane goma tare da yin awon gaba da wasu da dama kamar yanda Jaridar Solacebase ta ruwaito
Advertisements
