News
Babbar Magana: An Sace Wata Mata Mai Juna Biyu A Hanyar Zuwa Asibiti
DAGA UASIR SANI ABDULLAHI
An sace wata mata mai juna biyu mai suna Mrs Ogunbunmi a Abeokuta, babban birnin jihar Ogun.
Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa Matar wadda aka ce za ta haihu ta bar gidanta da ke Oke Lantoro zuwa babban asibitin jihar, Ijaiye dake Abeokuta,sai dai an yi garkuwa da ita a hanya.
Mijinta, Ogunbunmi Lateef, ya ce ya samu sakon WhatsApp da ke sanar da shi sace matarsa.
Kakakin rundunar ‘yan sandan, Omolola Odutola, ya tabbatar da faruwar lamarin amma bai yi cikakken bayani ba.
A cikin wata sanarwa da ta fitar, a ranar Alhamis, ta ce, “Wani Ogunbunmi Lateef na Oke Lantoro ya ruwaito cewa matarsa mai juna biyu da za ta haihu ta bar gida zuwa Asibitin Jihar Ijaiye Abeokuta.
Ogun na daya daga cikin jihar da ke fama da yawaitar laifuka a yankin Kudumaso Yamma.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
