News
Gwamatin Tarraya Ta Ware Naira Biliyan 155 Don Raba Abinci Ga Magidanta Da Bai Wa Kowannen Su Dubu 50
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ya tabbatar da shirin gina ƙasa da tallafawa magidanta a yayin wani zama da Majilisar kula da harkokin tattalin arziƙin ƙasa, NEC a Abuja.
Wani jawabi da ya fito daga ofishin mai magana da yawunsa, Ajuri Ngelale ya ce manufar shirin su ne dan a inganta harkokin noma da tattalin arziƙi gami da bada tallafi domin rage raɗaɗin talauci ga ƴan Najeriya.
Jaridar Punch ta ruwaito cewa Shirin wanda ya samu goyon bayan Majalisar ta NEC, ya ƙunshi rarraba kuɗaɗe da yin ayyukan more rayuwa a dukkan shiyyoyin ƙasarnan guda shida, inda za a bada tallafin naira dubu 50 ga iyalai 100,000 a kowace Jiha na tsawon watanni uku.
Ya ƙara da cewa gwamnatin ta ware naira biliyan 155 domin sayan kayan abinci da kuma raba su ga magidanta don samu sauki ta fuskar mallakar abinci a cikin al’umma.
Ngelale ya ce, shugaba Tinubu ya yi kira ga gwamnoni da su bada haɗin kai wajen ganin sun samar da buƙatun al’ummarsu da kuma inganta harkokin noma.
-
News5 days ago
ICPC Ta Yi Barazanar Daurin Shekaru 7 Ga Masu Yiwa Baki Rajistar NIN A Matsayin Yan Najeriya
-
News1 day ago
Jam’iyyar ADC Ta Yi Watsi Da Cire Ta Daga Rijista, Ta Sha Alwashin Kalubalantar Hukuncin Kotu
-
News6 days ago
Hayar Jirage Hadi Sirika Ya Dakko Daga Habasha Don Damfarar Yan Najeriya Da Sunan “Nigeria Air” — Shaida
