Connect with us

News

Gwamatin Tarraya Ta Ware Naira Biliyan 155 Don Raba Abinci Ga Magidanta Da Bai Wa Kowannen Su Dubu 50

Published

on

Shugaban Kasa Bola Ahmad Tunibu

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

 

Advertisement

Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ya tabbatar da shirin gina ƙasa da tallafawa magidanta a yayin wani zama da Majilisar kula da harkokin tattalin arziƙin ƙasa, NEC a Abuja.

Wani jawabi da ya fito daga ofishin mai magana da yawunsa, Ajuri Ngelale ya ce manufar shirin su ne dan a inganta harkokin noma da tattalin arziƙi gami da bada tallafi domin rage raɗaɗin talauci ga ƴan Najeriya.

Advertisement

Asibitin Best Choice Ya Fara Kula Da Masu Lalurar Mafitsara 

Jaridar Punch ta ruwaito cewa Shirin wanda ya samu goyon bayan Majalisar ta NEC, ya ƙunshi rarraba kuɗaɗe da yin ayyukan more rayuwa a dukkan shiyyoyin ƙasarnan guda shida, inda za a bada tallafin naira dubu 50 ga iyalai 100,000 a kowace Jiha na tsawon watanni uku.

Ya ƙara da cewa gwamnatin ta ware naira biliyan 155 domin sayan kayan abinci da kuma raba su ga magidanta don samu sauki ta fuskar mallakar abinci a cikin al’umma.

Advertisement

Ngelale ya ce, shugaba Tinubu ya yi kira ga gwamnoni da su bada haɗin kai wajen ganin sun samar da buƙatun al’ummarsu da kuma inganta harkokin noma.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending