Connect with us

News

Mutum Aƙalla Shida Ne Suka Mutu Bayan Wata ‘Yar Ƙunar-baƙin-wake Ta Tashi Bam A Taron Biki 

Published

on

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN 

Mutum aƙalla shida sun mutu bayan wata ‘yar ƙunar-baƙin-wake ta tashi bam da ke jikinta a ƙaramar hukumar Gwoza ta Jihar Borno da ke arewa maso gabashin Nijeriya ranar Asabar.

Advertisement

Kamfanin dillancin labaran News Agency of Nigeria (NAN), wanda ya ambato Kwamishinan ‘yan sandan Jihar Borno Yusuf Lawal yana tabbatar da aukuwar lamarin, ya ƙara da cewa mutum kimanin 15 ne suka jikkata.

Yaran Masu Faɗa Aji Ne Kaɗai Zasu Iya Samun Lamunin Karatu Da Gwamnatin Tarayya Za Ta Bayar —BUK Lecturer

Ganau sun ce matar, wadda ke goye da jariri, ta tashi bam ɗin ne a wani wurin biki a Marrarraban Gwoza.

Advertisement

NAN ya ambato wani ganau mai suna Muhammed Kasim yana cewa “mun ji babbar ƙarar fashewar wani abu da kuma tashin ƙura; sannan muka ga gangar jikin mutane a ƙasar.”

Ya ce an garzaya da mutanen da suka jikkata asibitin da ke Gwoza domin yi musu magani.

Advertisement

‘Kisa a maƙabarta’

Kazalika bayanai sun nuna cewa wani ɗan ƙunar-baƙin-waken ya tayar da bam a maƙabarta lokacin da aka je binne mutanen da suka rasu a harin bam na farko.

Advertisement

Mutumin, wanda ya saje a cikin masu jana’iza, ya kashe mutum ɗaya tare da jikkata wasu.

Tuni dai rundunar sojojin Nijeriya da ke aiki a yankin ta sanya dokar hana fita a Gwoza.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending