News
Yawan bashi : KEDCO Ta Yankewa Jami’ar aliko Dangote wutar lantarki
DAGA KABIR BASIRU FULATAN
Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Kano da Jigawa da Katsina (KEDCO) ya katse wutan lantarki na Jami’ar Aliko Dangote da ke Wudil, saboda basussukan da ake binta da ya kai har Naira miliyan ₦248m.
Alhaji Abubakar Yusuf, Manajan Daraktan KEDCO ne ya bayyana haka a wata tattaunawa ta wayar tarho da Kamfanin dillancin labarai na Nijeriya, NAN a yau Litinin, inda yace Naira miliyan ₦20m ne kacal jami’ar ta iya biya a cikin bashin.
Yusuf ya bayyana cewa KEDCO ba ta da wata mafita illa ɗaukar wannan tsattsauran mataki, inda ya jaddada mahimmancin jami’ar na biya kuɗin da ya kamata kafin a dawo da wutar lantarki.
Ya nanata matsayin kamfanin na cewa ba tare da biyan kudi ba, jami’ar za ta ci gaba da zama cikin duhu.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
