Connect with us

News

Firgici Ya Kunno Kai A Rano Da Ke Kano Bayan Da Wasu Masu Kama Da ‘Yan Daba Suka Mamaye Fadar Masarauta

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

 

Advertisement

Firgici ya kunno kai a Rano da ke Kano bayan da wasu masu kama da ‘yan daba suka mamaye fadar masarauta.

A cikin wata wasika da aka rubuta wa kwamishinan ‘yan sandan jihar kame yanda jaridar SolaceBase ta rawaito cewa ‘yan dabar sun yi sansani a fadar Sarkin Rano tun a ranar Lahadi da wasu da ba a tantance ko suwaye ba.

Advertisement

Sheikh Dahiru Usman Bauchi Ya Cika Shekaru 100 A Duniya

Ta ce har yanzu ba a san dalilan wadannan mutane masu dauke makamai ba, ana daukar zaman nasu a matsayin barazana ga tsaron rayuka da dukiyoyi al’ummar yankin.

A cewar wasikar, mazauna masarautar Rano mutane ne masu zaman lafiya da kullum suna gudanar da harkokinsu ba tare da haifar da tarzoma ba.

Advertisement

Ta ce a tsawon shekaru masarautar Rano ta samu zaman lafiya ba tare da wata matsala ba kuma hukumomin tsaro na iya shaida wannan tarihin da masarautar ke da shi.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending